ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT

Ƴan sanda sun tsare mutane 21

Kakakin ƴan sanda, Jimoh Moshood ya bayyana haka a Abuja a lokacin da ya gabatar da waɗanda ake zargi a gaban ƴan jarida.

Police IG, Ibrahim Idris

Ƴan Sandan Nijeriya a ranar Litinin, Maris 8, ta ce an kama mutane 21 waɗanda ake zargi game da  kashe-kashe da lalata dukiya a Ile Ife, Jihar Osun.

Kakakin ƴan sanda, Jimoh Moshood ya bayyana haka a Abuja a lokacin da ya gabatar da waɗanda ake zargi a gaban ƴan jarida.

Ya ba da sunayen su kamar haka, Eluwole Akeem, Kuburat Eluwole, Ayoola Abimbola, Bello Wahab, Taiwo Fakuwajo, Ademola Ademiluyi, Peter Omisope, Adefisan Isaac, Adelekan Kehinde da Elufisan Akintoye.

Sunayen sauran na kamar haka, Omisanmi Isaac, Olanrewaju Daniel, Seyi Akinyobo, Adejube Monday, Olanrewaju Adebayo, Akanbi Adeyinka, Obimankinde Samuel, Zakariyu Abdulyekini, Bamidele Elusanmi, Jimoh Sakiru da Clement Kehinde.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa, mutane 39 da ake zargi  aka kama bayan rikicin, aka saki 18 bayan bincike domin rashin shaida, a kansu.

Moshood ya ce, sauran 21 da aka kama, an gan su da laifin tsoma hannu kai tsaye a kisan mutane.

Ya lura da cewa  jami'an tsaro na musamman da aka tura zuwa Ile-Ife domin kwantar da rikicin ba su kama kowa da rashin la'aƙari ba, kamar yadda ake bayar da rahoton a wasu kafofin watsa labarai.

Ya ce rikicin ya fara a kan Maris 7 a lõkacin da ƙungiyoyin Yarabawa da Hausawa suka fara jefa wa juna duwatsu, waɗannan ake zargi da fara rikicin, Kuburat Eluwole da Abubakar Mohammed.

"An tarwatsa masu tarzoman, an kwantar da hankalin kowa da kowa"

ADVERTISEMENT

Ya nuna cewa ƴan sanda sun jira a gaban yankin Sabo a Ile-Ife har kashegari.

Ya shawarci sarakuna, da shugabannin addini, ƴan siyasa da kuma iyaye su goyi bayan ma'aikatan jami'ar tsaro na musamman a jihar.

Ya ce za a gurfanad da waɗanɗa aka kama a gaban shari'a a kan kammala bincike, yayin aka sake mutane 18.

Inspector General  na 'ƴan sanda, Mr Ibrahim Idris, ya tura' ƴan sanda (SIF) zuwa Ile-Ife, Osun, don mayar zaman lafiya a yankin

JOIN OUR PULSE COMMUNITY!

Unblock notifications in browser settings.
ADVERTISEMENT

Eyewitness? Submit your stories now via social or:

Email: eyewitness@pulse.ng

Recommended articles

Here's everything to know about being a virgin on your wedding night

Here's everything to know about being a virgin on your wedding night

7 do's and don’ts of the Holy month of Ramadan

7 do's and don’ts of the Holy month of Ramadan

Top 5 sweetest celebrity mother-child relationships that stand out for us

Top 5 sweetest celebrity mother-child relationships that stand out for us

International Women's Day: 5 Nigerian female celebrities championing women’s rights

International Women's Day: 5 Nigerian female celebrities championing women’s rights

Top 5 female directors in Nollywood

Top 5 female directors in Nollywood

6 things that will break a Muslim's fast during Ramadan

6 things that will break a Muslim's fast during Ramadan

5 benefits of fasting during Ramadan

5 benefits of fasting during Ramadan

5 reasons Easter was more fun when we were children

5 reasons Easter was more fun when we were children

Dos and don’ts of supporting Muslims during Ramadan

Dos and don’ts of supporting Muslims during Ramadan

ADVERTISEMENT
ADVERTISEMENT