Akalla an ruwaito mutane bakwai matattu bayan ƴan ta'adda guda uku sun kai farmaki a wani ƙauye a Maiduguri, Jihar Borno.
ADVERTISEMENT
An Kashe Uwa da ƴa'ƴan ta Biyu da nakiya a Jihar Borno
A lokacin da ƴan ta'addan suka gane cewa an gane su, sai suka watsa hanyoyi daban-daban, sannan suka tada na'urar dake maƙale a jikinsu yayin kan gudu.
Wata Uwa, ƴaƴanta biyu, da kuma wasu mutane huɗu sun rasu akan harin da ya faru a daren Asabar, Maris 18. An ce maharan sun yi yunƙurin shiga Maiduguri ta ƙauyen Umarari a Molai, inda ƴan Civilian Joint Task Force (CJTF) suka ƙalubanta su.
A lõkacin da suka gane cewa ya na yiwuwa an gane su, sai suka watse a hanyoyi daban-daban, suka tada nakiyoyin da ke maƙale a jikinsu yayin kan gudu.
Wasu mutane Takwas sun ji rauni a harin, su na ƙarbar magani a wani asibiti a garin.
JOIN OUR PULSE COMMUNITY!
ADVERTISEMENT
Eyewitness? Submit your stories now via social or:
Email: eyewitness@pulse.ng
ADVERTISEMENT